Thursday, 7 September 2017

Yadda Mata suke Hukunta Mazajensu A Legas

Yaki da Chin Hanci da Rashawa a Nigeria Kwalliya Ta Biya Kudin Sabulu
Saboda An Wayi Gari a Kasa Irin Nigeria An Samu Kudi an Rasa Mai Su Kowa Na Tsoron Yace Nashi Ne Domin Gudun Hushin Hukuma Wanda A Yan Shekarunan Bamu Taba Tsammanin Haka Zata Faruba
Sai Dai Muyi Godiya Ga Allah Mu Roki Allah Yakara Taimakon Wanan Gwamnatin Wajen Dawo Da Martaban Kasarmu Nigeria
Daga
Aliyu Abdullahi Malumfashi
Wednesday, 6 September 2017

Zai Dauki Lokaci Kafin Talakawa Su Fara Amfana Da Farfadowar Tattalin Arziki - NBS
Ya ce, fita daga kariyar tattalin arziki su ne matakin farko na kai wa ga samun sauki kuma dole dai dore a kan haka sannan za a kai ga nasara tare kuma da kauce sake komawa gidan jiya.

YADDA SAMA DA MUSULMAI DUBU TALATIN SUKAYI HIJIRA CIKIN KANKANIN LOKACI DAGA BURMA
Kabilar Rohingya dubu talatin da Bakwai ne, (37,000) suka tsere zuwa kasar Bangladesh cikin Awanni ashirin da hudu24 bayan irin kisar girlar da akeyi musu a kasar Burma

A Karo Na Biyu Buhari Ya Soke Zaman Majalisar Ministoci

2019: Ministar Harkokin Mata Ta Fara Yi Wa Atiku Kamfe
Ministar harkokin mata, Hajiya Aishatu Isma'ila ta soma yi wa tsohon mataimakin shugaban kasar Atiku Abubakar yakin neman zabe na shekarar 2019. Ministar, wacce ta jagoranci shugabannin jam'iyyar APC na jihar Taraba domin kai gaisuwar Sallah ga Atiku Abubakar, ta yi addu'ar Allah ya ba shi shugabancin kasar a 2019.
Wani bidiyo da jaridar Daily Nigerian wacce ake wallafawa a shafin intanet ta buga, ya nuna ministar a gaban tsohon mataimakin shugaban kasar tana cewa, "Your Excellency (mai girma), babanmu, shugaban kasarmu idan Allah ya yarda a shekarar 2019... a gabanka, mutanenka ne, magoya bayanka har abada; mutanen jihar Taraba.
"Sun zo gaisuwar ban-girma, gaisuwar Sallah da kuma yi maka murna ta wannan daukaka (Wazirin Adamawa) da Allah ya kara Minista Alhassan ya gabatarwa tsohon mataimakin shugaban kasar shugabannin jam'iyyar, tana mai cewa wasunsu sun matsa domin su yi jawabi a gabansa amma hakan ba zai yiwu ba saboda ya gaji.
Tawagar ta rika yin tafi a lokacin da ministar ke wadannan jawabai.
Ministar ta harkokin mata dai ita ce ta yi takarar gwamnan jihar Taraba a karkashin jam'iyyar APC a shekarar 2015, ko da yake ta sha kaye a hannun Gwamna mai-ci, Darius Ishaku na jam'iyyar PDP.

Ya Aka Yi Wannan Sirri Ya Bayyana?
Shakka babu da mamaki Minista ta rika kamfe ga wani saboda ya samu kujerar shugaban kasa da ya ba ta mukami. Shin ba ta yi farin ciki ba ne da mukamin ko kuwa ba ta samun abinda ya kamata da kujerar?
Shin a sirri aka yi wannan abu daga bisani asiri ya tonu? Ko kuwa tana zargin akwai sunanta a Ministoci da za a kora? Shin me ya sa take fatan Atiku ya karbi kujerar Buhari? Su wa suka saki faifan bidiyon?