Wednesday, 6 September 2017

YADDA SAMA DA MUSULMAI DUBU TALATIN SUKAYI HIJIRA CIKIN KANKANIN LOKACI DAGA BURMA



DAGA AUWAL M KURA
Kasa da awanni ashirin da hudu al-ummar Rohingya kusan Dubu Talatin da bakwai (37,000) suka tsere zuwa Bangladesh
Majalisar Dinkin Duniya ta ce akalla musulmai ‘yan
Kabilar Rohingya dubu talatin da Bakwai ne, (37,000) suka tsere zuwa kasar Bangladesh cikin Awanni ashirin da hudu24 bayan irin kisar girlar da akeyi musu a kasar Burma
Inda majalisar dinkin duniya ta Bayyana  lamarin da matsayin Gudun hijira mafi girma da aka Taba gani cikin karamin lokaci Tun bayan sabon tashin Hankalin da ya barke a kasar Myanmar .
A cewar Majalisar, wannan ta sa Yawan ‘yan kabilar Rohingya da suka tsere daga  burma zuwa Bangladesh ya karu zuwa dubu Dari da ashirin da biyar (125,000) daga dubu Casa’in (90,000)

A Karo Na Biyu Buhari Ya Soke Zaman Majalisar Ministoci



A karo na biyu tun bayan da ya dawo jinya daga waje, Shugaba Muhammad Buhari ya soke zaman majalisar ministoci wanda aka tsara gudanarwa a yau Laraba.
Ministan Yada Labarai, Lai Mohammed ya ce an soke zaman majalisar ce saboda rashin isasshen lokaci da ministocin za su nazari kan batutuwan da aka tsara tattaunawa a lokacin zaman sakamakon bukukuwan Babban sallah da aka gudanar.

2019: Ministar Harkokin Mata Ta Fara Yi Wa Atiku Kamfe


Ministar harkokin mata, Hajiya Aishatu Isma'ila ta soma yi wa tsohon mataimakin shugaban kasar Atiku Abubakar yakin neman zabe na shekarar 2019. Ministar, wacce ta jagoranci shugabannin jam'iyyar APC na jihar Taraba domin kai gaisuwar Sallah ga Atiku Abubakar, ta yi addu'ar Allah ya ba shi shugabancin kasar a 2019.

Wani bidiyo da jaridar Daily Nigerian wacce ake wallafawa a shafin intanet ta buga, ya nuna ministar a gaban tsohon mataimakin shugaban kasar tana cewa, "Your Excellency (mai girma), babanmu, shugaban kasarmu idan Allah ya yarda a shekarar 2019... a gabanka, mutanenka ne, magoya bayanka har abada; mutanen jihar Taraba.

"Sun zo gaisuwar ban-girma, gaisuwar Sallah da kuma yi maka murna ta wannan daukaka (Wazirin Adamawa) da Allah ya kara  Minista Alhassan ya gabatarwa tsohon mataimakin shugaban kasar shugabannin jam'iyyar, tana mai cewa wasunsu sun matsa domin su yi jawabi a gabansa amma hakan ba zai yiwu ba saboda ya gaji.

Tawagar ta rika yin tafi a lokacin da ministar ke wadannan jawabai.
Ministar ta harkokin mata dai ita ce ta yi takarar gwamnan jihar Taraba a karkashin jam'iyyar APC a shekarar 2015, ko da yake ta sha kaye a hannun Gwamna mai-ci, Darius Ishaku na jam'iyyar PDP.

Ya Aka Yi Wannan Sirri Ya Bayyana?



Shakka babu da mamaki Minista ta rika kamfe ga wani saboda ya samu kujerar shugaban kasa da ya ba ta mukami. Shin ba ta yi farin ciki ba ne da mukamin ko kuwa ba ta samun abinda ya kamata da kujerar?

Shin a sirri aka yi wannan abu daga bisani asiri ya tonu? Ko kuwa tana zargin akwai sunanta a Ministoci da za a kora? Shin me ya sa take fatan Atiku ya karbi kujerar Buhari? Su wa suka saki faifan bidiyon?

Sunday, 20 August 2017

Yadda Na Ji Rauni A film Din Dakin Amarya —Aisha Tsamiya

Fitacciyar jarumar nan ta fina-finan Kannywood, Aisha Aliyu, wacce aka fi sani da suna Aisha Tsamiya ta shaida wa wakilinmu cewa babu fim din da ya taba ba ta wahala kamar "Dakin Amarya".

Fim din Dakin Amarya yana magana ne kan yadda mata ke bakin kishi, musamman idan aka auro musu abokiyar zama - ta fito ne a matsayin kishiyar Halima Atete, wacce ita ce uwar gidan Ali Nuhu.
"Sai da na ji rauni na gaske a fim din musamman saboda yadda aka rika yin fatali da kayan daki irinsu tangaran da talabijin. Kai har kwanciya na yi a asibiti", in ji Aisha Tsamiya.
Jarumar ta kara da cewa tun tana karama take sha'awar fitowa a fina-finan Kannywood "saboda suna matukar burge ni".
A cewarta, "Na dauki yin fim a matsayin sana'a don haka ina jin dadin fitowa a cikinsa."
Tsamiya, wacce ta soma fim a shekarar 2011, ta kara da cewa dukkan jaruman da ke yin fim tare da ita suna burge ta "kuma ina zaune da kowannensu lafiya".
"Jarumai irinsu su Adamu (Adam A. Zango), Sadiq Sani Sadiq, Zahraddeen Sani, da dukkansu sauran jarumai suna burge ni. Haka ma mata jarumai, dukkansu ina zaune da su lafiya kuma suna burge ni", in ji Aisha Aliyu.
Ta ce ta soma fitowa a fim din Tsamiya ne shi ya sa aka sanya mata wannan suna.
Aisha dai ta fi fitowa a fina-finan da ke nuna ta a mutuniyar kirki, wacce kuma ake tauyewa hakki.

PDP ta lallasa APC a zaben Gombe


Jam’iyyar PDP ta doke APC a zaben cike gurbi da akayi na dan majalisar dokokin jihar Gombe jiya Asabar.Dan takaran kujeran dan majalisar Dukku na jam’iyyar PDP Sa’idu Malala ne ya lashe zaben da kuri’u sama da 7000 in da A Inuwa ya sami kuri’u 4000 da yan kai.

A watan Yunin da ya gabata ne Allah yayi wa dan Majalisar dokokin jihar da ke wakiltan karamar hukumar Dukku Gambo Kabade rasuwa.Jam’iyyu 7 ne suka  takara a zaben.

Saturday, 19 August 2017

Zan sallami Arsene Wenger daga Arsenal idan na siya kungiyar kwallon kafar – Dangote






Hamshakin attajiri, wanda ya fi kowa kudi a Afrika, Aliko Dangote, ya bayyana cewa, matsawar ya sayi hannun jarin kungiyar kwallon kafa ta Arsenal da ke Londan, farkon abin da zai fara yi shi ne sallamar mai horas da ‘yan wasa Arsene Wenger.Ya yi wannan bayani ne lokacin da ya ke zantawa da kafar yada labarai mai suna Bloomberg, inda ya kara da cewa, ya nan kan bakan sa na kokarin ganin cewa, da zaran ya kammala ginin matatar man fetur din sa a Legas, zai tuntubi mamallakin kulub din Arsenal, Stan Kroenke, domin sayen kungiyar.


Dangote, wanda darajar arzikin sa ta kai Fam Biliyan 8.6, ya dade ya na goyon bayan Arsenal. Tun cikin shekarun 1980 ya ke dan goyon bayan kungiyar.“Farkon abin da zan fara yi shi ne na sallami mai horas da yan wasan kungiyar. Ya yi rawar gani a tsawon shekarun da ya yi, amma akwai bukatar kawo wani domin shi ma ya jaraba ta sa sa’ar.” Haka Dangote ya shaida wa Bloomberg.Wenger dai ya shafe shekaru 21 ya na koyar da wasan kwallo a kungiyar Arsenal, wanda hakan ya kai shi ga zama wanda ya fi kowane mai horas da wasa dadewa a kungiya daya a kashashen Turai.