Saturday 19 August 2017

Home › › Zan sallami Arsene Wenger daga Arsenal idan na siya kungiyar kwallon kafar – Dangote

Subscribe Our Channe







Hamshakin attajiri, wanda ya fi kowa kudi a Afrika, Aliko Dangote, ya bayyana cewa, matsawar ya sayi hannun jarin kungiyar kwallon kafa ta Arsenal da ke Londan, farkon abin da zai fara yi shi ne sallamar mai horas da ‘yan wasa Arsene Wenger.Ya yi wannan bayani ne lokacin da ya ke zantawa da kafar yada labarai mai suna Bloomberg, inda ya kara da cewa, ya nan kan bakan sa na kokarin ganin cewa, da zaran ya kammala ginin matatar man fetur din sa a Legas, zai tuntubi mamallakin kulub din Arsenal, Stan Kroenke, domin sayen kungiyar.


Dangote, wanda darajar arzikin sa ta kai Fam Biliyan 8.6, ya dade ya na goyon bayan Arsenal. Tun cikin shekarun 1980 ya ke dan goyon bayan kungiyar.“Farkon abin da zan fara yi shi ne na sallami mai horas da yan wasan kungiyar. Ya yi rawar gani a tsawon shekarun da ya yi, amma akwai bukatar kawo wani domin shi ma ya jaraba ta sa sa’ar.” Haka Dangote ya shaida wa Bloomberg.Wenger dai ya shafe shekaru 21 ya na koyar da wasan kwallo a kungiyar Arsenal, wanda hakan ya kai shi ga zama wanda ya fi kowane mai horas da wasa dadewa a kungiya daya a kashashen Turai.

No comments:
Write comments