Saturday, 9 September 2017

An daidaita tsakanin malaman Jami'o'i da gwamnatin tarayya
Kungiyar Malaman Jam'i'o'i ta Kasa, ta amince da yarjejeniyar da ta cimma a zamanta da gwamnatin tarayya, inda ta yarda za ta janye yajin aiki da zarar uwar kungiyar ta amince gaba dayan su.
A cimma wannan yarjejeniya ce bayan malaman sun shafe sa'o'i 12 da rabi su na tattaunawa an Abuja.
Har ila yau, a yayin wannan dogon zama da otherwise known as yi, a kuma kafa kwamiti mai kunshe da mutane bakwai a bangaren gwamnati da na bakwai a bangaren malaman Jami'o'in da zu duba yadda gwamnati za ta yi aiki da yarjejeniyar 2009, wacce dama rashin aiki da ita ne ya haifar da yajin aikin.
Kamar yadda Ministan Kwagago, Chris Ngige ya bayyana, ya ce kwamitin zai kunshi wakilai uku daga Ma'aikatar Ilmi, wasu uku daga Kungiyar Malaman Jami'o'i ta Kasa, sai kuma wakili daya daga bangaren Gwamnartin Tarayya, wanda shi ne zai kasance shugaban kwamiti.
Shugabannin kungiyar sun bayyana cewa duk da dai sun amince da yarjejeniyar, za su mika tayin da gwamnati ta yi musu, wurin mambobin su, daga nan bayan sati daya kuma su waiwayi gwamnatin tarayya dangane da matsayar su.
Shugaban kungiyar na kasa, Biodun Ogunyemi, ya shaida wa manema labarai cewa za su koma su tuntubi uwar kungiyar su gaba daya, daga nan kuma bayan mako guda su tunkari gwamnati da abin da su ka zartas.
A nasa bangaren, Ministan Ilmi, Adamu, ya ce a yarda za a biya wa kungiyar bukatun ta, kuma za su janye yajin aiki nan da mako guda bayan sun tuntubi sauran daukacin mambobinsu na fadin kasar nan.
A dai fara tattaunawar damisalin 1:38 na ranar Alhamis, otherwise known as kammala karfe 2:15 na daren Juma'a.
Friday, 8 September 2017

Mata uku wadanda suka zamo Sanannu a Arewa na daya zata baka mamaki
Fitacciyar jarumar nan ta wasan kwaikwayon Hausa da turanci wato ta Kannywood da Nollywood Rahama Sadau ta shiga cikin jerin mata uku sa suka fi tashe a harkar fina-finai da nishadantarwa a yankin mu na arewacin Nigeria
Jaridar Thisday ce dai ta wallafa sunaye gami da hotunan wadannan yan mata a shafinsu na instagram inda suka ayyana su a matsayin manya mata kuma masu tashe a bangaren nishadantarwa a arewa.
Wadannan shahararrun mata dai sune babbar mawakiyar nan Hadiza Blell wacce aka fi sani da suna Dija. Da kuma fitacciyar mai gabatar da shiri a gidan television wato Salma Phillips. Sai kuma jarumar wasan kwaikwayon Hausa Rahama Sadau.

Hotunan sabuwar motor da dan wasan Real Madrid ya siya
Dan wasan Real madrid Cristiano Ronaldo ya samu karuwa cikin jerin motocin da ya tara masu tsada.
Zakaran yan ƙwallon turai ya dora hoton motar wanda kimanin ta ta kai N162M (£350,000) a shafin shi na instagram.
A cikin hoton Cristiano ya tsaya kusa da motar.
Motar kerar Ferarri (Ferarri F12TDf) ne kuma ya shiga cikin jerin motocin da dan kwallon ke da shi.
Cikin jerin motoci masu tsada da dan wasan Real madrid ya tara akwai Porsche 911 Turbo S, Bently GT Speed, Bentley Continental GTC, Ferrari 599 GTB Fiorano, Rolls Royce Phantom Drophead Coupe, Ferrari F430, Koenigsegg CCX da sauransu.
Ya siyo sabon motar bayan ya taimaka ma tawagar yan ƙwallon ƙasar Portugal wajen cin nasara a wasan share fage na buga gasar kofin duniya inda suka gama da kasar Hungary da Faroe Island.
Dan wasan zai koma ga tawagar Real madrid amma ba zai buga wasan su da Levante ranar asabar 9 ga watan Satumba sanadiyar dakatarwa da aka bashi.

Video: Yadda maza suke shigar mata suna aikata kwartanci
Wannan video da kuke gani a kasa wani namiji aka kamashi dashigar mata yayinda yai kokarin shiga gidan wata matar aure
Ga Dai Video Nan Kuyi Download Ku Kallah Kuma Ku Saurara Yadda Abun Ya Kasance Dashi Tsakanin Wadanda Suka Kamashi.
Ga Dai Video Nan Kuyi Download Ku Kallah Kuma Ku Saurara Yadda Abun Ya Kasance Dashi Tsakanin Wadanda Suka Kamashi.
Thursday, 7 September 2017

Yadda Mata suke Hukunta Mazajensu A Legas
Gwamnatin jihar Lagos da ke Najeriya ta ce tana samun karin rahotannin da ke nuna mata na lakadawa mazajensu duka a jihar.
Kwamishinan shari'a na jihar Mr Adeneji Kazeem ya ce sun samu rahotanni da dama daga wurin mazajen da ke shan dan banzan duka daga wurin matansu, yana mai bayyana lamarin da cewa ya yi muni.
Ita ma shugabar hukumar yaki da cin zarafin mutane ta jihar, Misis Lola Adeniyi, ta shaida wa BBC cewa, "Ma'aurata maza 55 sun kawo karar matansu inda suke zargin sanya su cikin halin damuwa da furta bakaken maganganu da kuma lakada musu duka".
"Akwai uku da suka ce matansu sun yi musu dukan kawo-wuka, biyu daga cikinsu sun ce suna da shaida hotuna da ke nuna hakan; da yawa daga cikinsu suna so hukuma ta warware matsalolin ba tare da an kai kararsu a gaban kotu ba. Wasu mazajen kuma suna so ne a kai su asibit domin yi musu magani", in ji shugabar
Ba kasafai dai ake samun labarin kan yadda mata ke dukan maza ba.
Sai dai wata mata ta shaida wa BBC cewa tura ce ta kai bango shi ya sa muke yin raddi.
Ta kara da cewa, "Babu mamaki cin zarafin da maza ke yi wa mata a gida ne ya yi yawa shi ya sa matan su ma suke lakadawa mazajensu nasu duka. Ka san idan tura ta kai bango ba ka da mafita idan baka tashi ka kare kanka ba".

Yaki da Chin Hanci da Rashawa a Nigeria Kwalliya Ta Biya Kudin Sabulu
Saboda An Wayi Gari a Kasa Irin Nigeria An Samu Kudi an Rasa Mai Su Kowa Na Tsoron Yace Nashi Ne Domin Gudun Hushin Hukuma Wanda A Yan Shekarunan Bamu Taba Tsammanin Haka Zata Faruba
Sai Dai Muyi Godiya Ga Allah Mu Roki Allah Yakara Taimakon Wanan Gwamnatin Wajen Dawo Da Martaban Kasarmu Nigeria
Daga
Aliyu Abdullahi Malumfashi
Wednesday, 6 September 2017

Zai Dauki Lokaci Kafin Talakawa Su Fara Amfana Da Farfadowar Tattalin Arziki - NBS
Ya ce, fita daga kariyar tattalin arziki su ne matakin farko na kai wa ga samun sauki kuma dole dai dore a kan haka sannan za a kai ga nasara tare kuma da kauce sake komawa gidan jiya.
Subscribe to:
Posts (Atom)